Littafi Mai Tsarki Kwatanta

1
Yesu ya shiga jirgin ruwa, ya ƙetare ya zo garinsa.
2
Waɗansu mutane suka kawo masa wani shanyayye, kwance a tabarma. Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce wa shanyayyen, “Kada ka damu saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
3
Da jin wannan, waɗansu malaman dokoki suka ce wa juna, “Wannan mutum yana yin saɓo!”
Hausa Bible 2020
Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ Neman Rubutaccen Izini 2009, 2020 ta hannun Biblica, Inc. An yi amfani da izinin Biblica, Inc. Neman izinin nan ya game dukan Duniya. Hausa Contemporary Bible™ 2009, 2020 by Biblica, Inc.
1
سَيْ عِيسَىٰ يَشِغَ جِضْغٍ ضُوَ، يَهَيٜىٰ تٜىٰكُنْ يَجٜىٰ كَڢَرْنَهُمْ، غَرِنْ دَ يَيِ غِرْمَ؞
2
سَيْ عَكَ كَٰوُاْ مَسَ وَنِ شَنْيَيّٜىٰ يَنَ ݣُونْثٜىٰ عَكَنْ تَبَرْمَ؞ دَ عِيسَىٰ يَغَ بَنْ‌غَسْكِيَرْسُ، سَيْيَثٜىٰ وَشَنْيَيّٜىٰنْ «كَدَ كَدَامُ، طَانَ، أَنْ‌غَاڢَرْتَا مَكَ ذُنُبَنْكَ؞»
3
دَجِنْ وَنَّنْ، وَطَنْسُ مَلَمً كُواْيَرْوَرْ مُوسَٰى سُكَثٜىٰ وَجُونَنْسُ «وَنَّنْ مُتُمِنْ يَنَيِ وَ اللَّهْ صَاٻُواْ؞»
Hausa Bible Arabic 2020
Hausa Common Language Ajami Bible The Bible Society of Nigeria, 2020
1
Da ya shiga jirgi, ya haye ya je garinsu.
2
Sai aka kawo masa wani shanyayye, kwance a gado. Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce wa shanyayyen, “Ɗana, ka yi farin ciki, an gafarta maka zunubanka.”
3
Sai waɗansu malaman Attaura suka ce a ransu, “Wannan mutum, ai, saɓo yake!”
Hausa Bible 1979
@ Bible Society of Nigeria 1979