Littafi Mai Tsarki Kwatanta
- |
|---|
| 1 |
| Yesu ya shiga jirgin ruwa, ya ƙetare ya zo garinsa. |
| 2 |
| Waɗansu mutane suka kawo masa wani shanyayye, kwance a tabarma. Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce wa shanyayyen, “Kada ka damu saurayi, an gafarta maka zunubanka.” |
| 3 |
| Da jin wannan, waɗansu malaman dokoki suka ce wa juna, “Wannan mutum yana yin saɓo!” |
| Hausa Bible 2020
Littafi Mai Tsarki, Sabon Rai Don Kowa™ Neman Rubutaccen Izini 2009, 2020 ta hannun Biblica, Inc. An yi amfani da izinin Biblica, Inc. Neman izinin nan ya game dukan Duniya. Hausa Contemporary Bible™ 2009, 2020 by Biblica, Inc. |
| 1 |
| سَيْ عِيسَىٰ يَشِغَ جِضْغٍ ضُوَ، يَهَيٜىٰ تٜىٰكُنْ يَجٜىٰ كَڢَرْنَهُمْ، غَرِنْ دَ يَيِ غِرْمَ؞ |
| 2 |
| سَيْ عَكَ كَٰوُاْ مَسَ وَنِ شَنْيَيّٜىٰ يَنَ ݣُونْثٜىٰ عَكَنْ تَبَرْمَ؞ دَ عِيسَىٰ يَغَ بَنْغَسْكِيَرْسُ، سَيْيَثٜىٰ وَشَنْيَيّٜىٰنْ «كَدَ كَدَامُ، طَانَ، أَنْغَاڢَرْتَا مَكَ ذُنُبَنْكَ؞» |
| 3 |
| دَجِنْ وَنَّنْ، وَطَنْسُ مَلَمً كُواْيَرْوَرْ مُوسَٰى سُكَثٜىٰ وَجُونَنْسُ «وَنَّنْ مُتُمِنْ يَنَيِ وَ اللَّهْ صَاٻُواْ؞» |
| Hausa Bible Arabic 2020
Hausa Common Language Ajami Bible The Bible Society of Nigeria, 2020 |
| 1 |
| Da ya shiga jirgi, ya haye ya je garinsu. |
| 2 |
| Sai aka kawo masa wani shanyayye, kwance a gado. Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce wa shanyayyen, “Ɗana, ka yi farin ciki, an gafarta maka zunubanka.” |
| 3 |
| Sai waɗansu malaman Attaura suka ce a ransu, “Wannan mutum, ai, saɓo yake!” |
| Hausa Bible 1979
@ Bible Society of Nigeria 1979 |